Kamfanin Dillancin Labarai na Ahlul-Bayt (a.s) - ABNA – ya bayar da rahoton cewa: Kamfanin dillancin labarai na "Nun" na Iraki, ya kawo cewa: Ali Falih al-Zaidi, firayim ministan Iraki, yana da niyyar, amsa gayyatar shugaban Iran Masoud Pezeshkian, domin ziyara a hukumce zuwa Tehran a mako mai zuwa.
Kuma wannan ziyara, a cewar rahoton, tana da nufin ƙarfafa dangantakar tsakanin Bagadaza da Tehran, da kuma tattauna batutuwan da suka shafi bangarorin biyu.
Kuma majiyoyin yada labarai na Iraki ba su bayyana cikakken bayani game da jadawalin hukuma ko tsawon wannan ziyara ba.
Firayim ministan Iraki a halin yanzu yana kan ziyara a hukumce a Amurka, inda yake gudanar da jerin tarurruka da jami'an Amurka game da dangantakar tsakanin kasashen biyu, hadin gwiwar tsaro da tattalin arziki, da kuma wasu batutuwan yanki da na duniya.
Kuma masu lura da al'amuran siyasa suna ganin cewa daidaituwar ziyarar al-Zaidi zuwa Tehran kai tsaye bayan Washington, yana nuna ƙoƙarin Iraki na taka rawar "gadar kulla alaka," da kuma kiyaye daidaito tsakanin manyan ƙasashen yanki da na duniya, da kuma shawo kan tashin hankali ko isar da sakonnin tsaro a cikin rikice-rikicen baya-bayan nan.
Shin Menene Ra’aynu Ga Wannan Ziyarar?
……………….
Ra'ayinka